Yan Nigeria na sukar EFCC kan rufe asusun Fayose
-Hukumar hana yima tattalin arzikin kasa zagon kasa watau EFCC a takaice ta dakatarda Fayose da wasu mukarrabansa taba asusunsu dake wasu bankuna.
– Yan Nigeria masu saurin fadin ra’ayinsu suna masu cewa sai hukumar ta nuna izinin yin hakan
Gwamna Ayodele Fayose na jihar Ekiti
Wand Kotu ta bata ko kuma ta daina yin abubuwa ba bisa ka’ida ba. Hukumar ta maida martani da cewa tana da ‘yancin dakatarda ko wane asusun banki wanda take zargi. An samu labarin dakatarda asusun gwamnan Jihar Ekiti a ranar 20 ga Yuni, 2016.
Yayin da yake maida martani, Fayose, ya zargi hukumar da karya doka wajen kokarinta da yaki da cin hanci da rashawa. Fayose ya ambaci sashe na 308 na kundin mulkin Nugeria na shekara 1999 da cewa ya bashi rigar kariya daga hukumci a matsayinsa na gwamna mai ci.
Hukumar dai na mai cewa rigar kariya bata hana ta binciken ko wane asusu ba ko da na gwamnnoni ne. ‘Yan Nigeria da dama suna nuna shakkun halarcin matakin da hukumar ta dauka, saboda tsarin mulki na kasa ya ba gwamnoni rigagar kariya.
KU KARANTA: Muna rokon Fayose ya ceci rayukan mutane Jihar Ekiti- APC
Wasu kuma suna goyon bayan hukumar da cewa Fayose ya cika sukar gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari. Wasu kuma suna tambayar ko hukumar ta samo izinin kotu kafin ta dakatarda asusun.
The post Yan Nigeria na sukar EFCC kan rufe asusun Fayose appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers.